Exodus 8:9 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ مُوسَٰى يَثٜىٰ وَ ڢِرْعَوْنَ «أَيْ، نَا يَرْدَ؞ كَيْ نٜىٰ ذَاكَ ذَاٻَا؞ أَوَنٜىٰ لُواْكَثِ نٜىٰ ذَنْ ضُواْڧِ يَهْوٜىٰهْ دُواْمِنْكَ دَ دَتَّاوَنْكَ دَ جَمَعَرْكَ دُواْمِنْ عَكَوَرْدَ ݣُوطِ دَغَ وُرِنْكُ دَ غِدَاجٜىٰنْكُ، سَيْدَيْ كُواْ نَثِكِنْ كُواْغِنْ نِلُ ذَاسُ ضَغٜىٰ؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Musa ya ce wa Fir'auna, “In ka yarda, a wane lokaci ne kake so in roƙa maka, kai da barorinka da jama'arka domin a kawar da kwaɗin daga gidajenku, a hallakar muku da su, sai dai na cikin Kogin Nilu za a bari?”