Ezekiel 11:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ رُوحُ يَطَغَنِ يَكَٰوُاْنِ عَڧُواْڢَرْ غَبَسْ تَغِدَنْ يَهْوٜىٰهْ وَدَّ تَكٜىٰ ڢُسْكَنْتَرْ غَبَسْ؞ عَبَاكِنْ ڧُواْڢَرْ شِغَ سَيْغَا مُتُمْ عَشِرِنْ دَ بِيَرْ؞ عَثِكِنْ وَطَنْدَ نَغَنِ، نَغَ يَعَظَنِيَ طَنْ أَظُّرْ دَ ڢٜىٰلَتِيَ طَنْ بٜىٰنَيَ، شُوغَبَنِّنْ جَمَعَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Ruhu ya ɗaga ni sama, ya kai ni ƙofar gabas ta Haikalin Ubangiji wadda dake fuskantar gabas. Sai ga mutum ashirin da biyar a bakin ƙofar. A cikinsu na ga Yazaniya ɗan Azzur, da Felatiya ɗan Benaiya, shugabannin jama'a.