Ezekiel 12:23 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.’ Ka ce musu, ‘Kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَبُواْدَ حَكَ كَڢَطَا مُسُ، كَثٜىٰ، ‹إِنْجِنِ عُبَنْ‌غِجِ يَهْوٜىٰهْ ذَنْ كَٰوُاْ ڧَرْشٜىٰنْ وَنَّنْ كَرِنْ مَغَنَ، بَذَاسُ ڧَارَ يِنْ أَمْڢَانِ دَ وَنَّنْ كَرِنْ مَغَنَرْ عَ إِسْرَٰٓءِيلَ بَ؞ عَمَّا كَڢَطَا مُسُ ثٜىٰوَ ݣُونَكِے سُنْيِ كُسَ عِنْدَ ذَاعَ تَبَّتَرْ دَ ثِكَاوَرْ كُواْوَثٜىٰ رُعُيَ؞›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ka faɗa musu, ka ce ni Ubangiji Allah na ce zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra'ila ba. Amma ka faɗa musu, cewa kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.