Ezekiel 13:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ڧَضْيَا سُكٜىٰ غَنِ، أَنَّبْثِنْ ڧَضْيَا سُكٜىٰيِ ثٜىٰوَ ‹إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ،› كُواْدَيَكٜىٰ يَهْوٜىٰهْ بَيْ عَيْكٜىٰسُ بَ، دُكْدَهَكَ سُنْسَا ذُوثِيَا غَ غَنِنْ ثِكَاوَرْ مَغَنَرْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Suna faɗar ƙarya, suna kuma yin duban ƙarya, suna cewa, ‘Ubangiji ya ce,’ alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba, duk da haka sun sa zuciya ga cikawar maganarsu.