Ezekiel 14:7 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“ ‘Duk sa’ad da mutumin Isra’ila ko baƙo mai zama a Isra’ila ya rabu da ni ya kuma kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuna sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi don yă neme ni, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مَيْ يِوُوَ وَنِ مُتُمِنْ غِدَنْ إِسْرَٰٓءِيلَ كُواْ وَنِ بَڧُوانْ دَيَكٜىٰ ذَمَ عَثِكِنْ جَمَعَرْ إِسْرَٰٓءِيلَ ذَيْ رَبُ دَنِے، يَكُمَ بَادَ كَنْسَ غَ بَوْتَرْ غُمَكَ؞ مَيْ يِوُوَ يَكُمَ مِيڧَ كَيْ غَ أَبِنْ تُنْتُٻٜىٰ وَنْدَ يَسَا يَيِ لَيْڢِے، عَمَّا دُكْدَهَكَ يَذُواْ وُرِنْ أَنَّبِے دُواْمِنْ يَنٜىٰمِ نُڢِينَ؞ عِدَنْ وَنِ يَيِ حَكَ ڢَا، نِے يَهْوٜىٰهْ دَكَيْنَ ذَنْ سَاكَ مَسَ!
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“‘Gama duk wanda yake na Isra'ila da dukan baƙin da suke baƙunta cikin Isra'ila, wanda ya rabu da ni, ya manne wa gumakansa, ya sa abin tuntuɓe a gabansa, sa'an nan ya zo yana roƙona a wurin annabi, ni Ubangiji zan sāka masa.