Ezekiel 16:8 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“ ‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
« ‹سَعَدَّ نَسَاكٜىٰ وُثٜىٰوَ كُسَدَكٜىٰ، سَيْ نَدُوبٜىٰكِ، غَاشِ كِنْ كَيْ لُواْكَثِنْ دَ ذَاعَ ڧَوْنَثٜىٰكِ؞ سَيْ نَرُڢٜىٰكِ دَ ذَنٜىٰنْ رُڢُوَتَ، نَرُڢٜىٰ ڟِرَيْثِنْكِ؞ نَشِغَ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ دَكٜىٰ حَرْ دَ ضَنْڟُوَا، كِنْ كُوَ ذَمَ تَاوَ؞ نِے عُبَنْ‌غِجِ يَهْوٜىٰهْ نَا ڢَطَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Sa'ad da na sāke wucewa kusa da ke, na dube ki, ga shi, kin kai lokacin da za a ƙaunace ki, sai na yafe miki tufata, na rufe tsiraincinki, na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, ni Ubangiji Allah na faɗa.