Ezekiel 20:21 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“ ‘Amma ’ya’yan suka yi mini tawaye. Ba su bi ƙa’idodina ba, ba su kula su kiyaye dokokina ba, ko da yake mutumin da ya kiyaye su zai rayu ta wurinsu, suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a hamada.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
« ‹عَمَّا یَیَنْسُ سُكَ تَيَرْ مِنِ، بَسُيِ تَڢِيَ بِسَغَ ڧَٰعِدُواْدِنَبَ، بَسُ لُورَ سُكِيَايٜىٰ عُمَرْنَيْنَبَ، وَطَنْدَ عِدَنْ مُتُمْ يَكِيَايٜىٰسُ، ذَيْ رَايُ؞ سُكَيِ بَنْظَ دَ رَانَرْ هُوتُ تَمَكُواْ تَاوَ؞ « ‹سَيْ نَيِ تُنَانِ ثٜىٰوَ ذَنْ ظُبَ ذَاڢِنْ ڢُشِنَ عَكَنْسُ، إِنْ غَمَ ڢُشِنَ عَكَنْسُ عَثِكِنْ دَاجِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Amma 'ya'yansu suka tayar mini, ba su kiyaye dokokina da ka'idodina ba, waɗanda idan mutum ya kiyaye su, zai rayu. Suka kuma ɓata ranar Asabar ɗina. Sai na yi tunani zan zubo musu da hasalata, in aukar da fushina a kansu a jeji.