Ezekiel 20:6 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A ranar na yi musu rantsuwa cewa zan fitar da su daga Masar zuwa ƙasar da na samo musu, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ رَانَرْ نَنْ نَيِمُسُ ضَنْڟُوَا ثٜىٰوَ ذَنْ ڢِتُواْ دَسُو دَغَ ڧَسَرْ مَصَرْ، إِنْ كَٰوُاْسُ ثِكِنْ ڧَسَرْدَ نَذَاٻَا مُسُ، ڧَسَاثٜىٰ مَيْ أَمْڢَانِ، ڧَسَرْ دَتَڢِے دُكَنْ ڧَسَاشٜىٰ أَلْبَرْكَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
a ran nan na rantse musu, cewa zan fito da su daga ƙasar Masar, zuwa wata ƙasa wadda na samo musu, ƙasar da take da yalwar albarka, wato ƙasa mai albarka duka.