Ezekiel 20:7 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Na kuma ce musu, “Kowannenku ya zubar da mugayen siffofin da kuka kafa idanunku a kai, kuma kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ نَثٜىٰمُسُ «كُواْوَنّٜىٰنْكُ يَكَوَرْدَ أَبُبُوَنْ ڧَظَنْتَا نَشَعَوَرْ عِدَنُونْسَ، كَدَ وَنِ يَڧَظَنْتَرْدَ كَنْسَ دَ غُمَكَنْ مَصَرْ؞ نِنٜىٰ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai na ce musu, ‘Bari kowane ɗayanku ya yi watsi da abubuwan banƙyama da kuke jin daɗinsu, kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masarawa, gama ni ne Ubangiji Allahnku.’