Ezekiel 21:7 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Kuma sa’ad da suka tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Domin labarun da suke fitowa. Kowace zuciya za tă narke kowane hannu kuma ya gurgunta; kowane ruhu zai sume kowane gwiwa kuma ta rasa ƙarfi kamar ruwa.’ Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَدَّ سُكَثٜىٰ، ‹دُوانْمٜىٰ كَكٜىٰ مَكُواْكِ؟› سَيْ كَثٜىٰ، ‹سَبُواْدَ لَابَرِنْ أَبِنْدَ يَكٜىٰ ذُوَا نٜىٰ؞ ذُوثِيَارْ كُواْوَ ذَاتَ نَرْكٜىٰ، حَنُّنْ كُواْوَ ذَيْ مُتُ، رُوحٌ كُواْوَ كُمَ ذَيْ سُومَ، ڠُوِوُاْيِنْ كُواْوَ ذَاسُيِ سَنْيِ كَمَرْ ضُوَ؞› غَاشِ، أَبِنْ يَنَ ذُوَا، ذَيْ تَبَّتَا؞ نِے عُبَنْغِجِ يَهْوٜىٰهْ نَا ڢَطَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Idan sun tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Saboda labarin abin da yake zuwa. Sa'ad da ya zo, kowace zuciya za ta narke, hannuwa duka za su yi suwu, kowane ruhu kuma zai suma, gwiwoyi duka kuwa za su rasa ƙarfi kamar ruwa. Ga shi, abin yana zuwa, zai tabbata,’ ni Ubangiji Allah na faɗa.”