Ezekiel 24:21 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku. ’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْيِ مَغَنَ دَ غِدَنْ إِسْرَٰٓءِيلَ ثٜىٰوَ ‹إِنْجِنِ عُبَنْغِجِ يَهْوٜىٰهْ ، ذَنْيِ بَنْظَ دَ وُرِينَ مَيْ ڟَرْكِے، أَبِنْ تَاڧَمَرْكُ، أَبِنْدَ كُكَڢِ ڧَوْنَ، أَبِنْدَ كُمَ يَكٜىٰ ڢَرَنْتَ مُكُ ذُوثِيَا؞ یَیَنْكُ مَظَا دَ مَاتَا وَطَنْدَ كُكَ بَرْسُ عَبَايَ، ذَاعَ كَشٜىٰسُ دَ تَكُواْبِے؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
in faɗa wa mutanen Isra'ila, cewa Ubangiji Allah ya ce, ‘Zan ƙazantar da Haikalina, abin fariyarku, da abin da idanunku suke jin daɗin ganinsa, da abin faranta zuciyarku. 'Ya'yanku maza waɗanda kuka bari a baya, za a kashe su da takobi.