Ezekiel 26:8 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zai kashe mazaunan filin ƙasar da takobi; zai yi miki ƙawanya, ya gina miki mahaurai, sa’an nan ya rufe ki da garkuwoyi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«مُتَنٜىٰنْ ڧَوْيُكَ نَڢِيلِنْ ڧَسَرْتَ كُمَ، ذَيْ هَلَّكَرْ دَسُو دَ تَكُواْبِے؞ ذَيْ تَادَ أَبُبُوَنْ هَوْرَ كَتَنْغَ دُواْمِنْ يَاڧِ، ذَيْ تَارَ ڧَسَا دُواْمِنْ يَهَوْ تَكَتَنْغَرْ بِرْنِ، ذَيْ تَادَ غَرْكُوُاْيِنْ غَابَا عَكَنْكِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Zai kashe ya'yanki mata waɗanda suke a filin ƙasar da takobi. Zai kuma kewaye ki da garun yaƙi, ya gina miki mahaurai, sa'an nan zai rufe ki da garkuwoyi.