Ezekiel 28:26 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذَاسُ ذَوْنَ لَاڢِيَ عَثِكِنْتَ، ذَاسُ غِنَا غِدَاجٜىٰ، سُيِ شُوكٜىٰ شُوكٜىٰنْ غُواْنَكِنْ إِنَبِے؞ ذَاسُ ذَوْنَ لَاڢِيَ سَعَدَّ نَحُكُنْتَ دُكَنْ مَڨُوبْتَنْ دَ سُكَ وُلَڧَنْتَسُ أَدَا؞ سَعَنً ذَاسُسَنِ ثٜىٰوَ نِنٜىٰ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْسُ؞› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Za su zauna lafiya a cikinta, za su gina gidaje, su yi gonakin inabi. Za su zauna gonakin inabi. Za su zauna lafiya sa'ad da na hukunta maƙwabtansu waɗanda suka wulakanta su. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji Allahnsu.’ ”