Ezekiel 29:19 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَبُواْدَ حَكَ، إِنْجِنِ عُبَنْغِجِ يَهْوٜىٰهْ ، ذَنْبَا سَرْكِے نٜىٰبُكَدْنٜىٰزَّرْ نَ بَابِيلَ ڧَسَرْ مَصَرْ، ذَيْ ݣُوشِ أَرْزِڧِنْتَ، يَلَلَتَرْدَ عِتَ، يَكُمَ ڨُوثٜىٰ أَبِنْدَ تَكٜىٰدَشِ؞ تَهَكَ ذَيْسَامِ أَبِنْدَ ذَيْبِيَ سُواْجُواْجِنْسَ وَهَلَرْ دَسُكَشَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Domin haka Ubangiji Allah ya ce, “Zan ba Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ƙasar Masar, zai kwashe dukiyarta, ya lalatar da ita, ya washe ta ganima. Za ta zama abin biyan sojojinsa.