Ezekiel 33:25 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kun ci nama da jini a cikinsa kuka kuma bauta wa gumakanku kuka zub da jini, kuna gani za ku mallaki ƙasar?
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَبُواْدَ حَكَ، غَ أَبِنْدَ نِے عُبَنْغِجِ يَهْوٜىٰهْ نَثٜىٰ، ‹تُنْدَ كُنَ ثِنْ نَامَ دَ جِنِنْسَ، كُنَ كَڢَ عِدَنُونْكُ غَ غُمَكَنْكُ، كُنَ كُمَ ظُبْدَ جِنِ، أَغَنِنْكُ ذَاكُ مَلَّكِ ڧَسَرْ؟
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Domin haka, sai ka faɗa musu, ‘Ubangiji Allah ya ce, “Kuna cin nama da jininsa, kuna bautar gumaka, kuna kuma yin kisankai, da haka za ku mallaki ƙasar?