Ezekiel 37:23 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَذَاسُ ڧَارَ ڧَظَنْتَرْ دَكَنْسُ دَ غُمَكَ دَ أَبُبُوَنْسُ نَڧَظَنْتَبَ؞ بَكُوَ ذَاسُ ڧَارَ ڧَظَنْتَرْ دَكَنْسُ دَ ذُنُوبِنْ غَنْغَنْثِنْسُبَ؞ ذَنْثٜىٰثٜىٰسُ دَغَ دُكَنْ كَوْثٜىٰوَرْ دَسُكَ ڢَاطِ عَثِكِ، إِنْكُمَ ڟَبْتَثٜىٰسُ؞ ذَاسُ ذَمَ مُتَنٜىٰنَ، نِے كُمَ ذَنْ ذَمَ اللَّهْ نْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da abubuwan banƙyama da kowane irin laifi ba. Zan komo da su daga riddar da suka yi, in tsarkake su. Za su zama jama'ata, ni kuma zan zama Allahnsu.