Ezekiel 38:13 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sheba da Dedan da ’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?” ’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
شٜىٰبَ دَ دٜىٰدَنْ دَ یَنْ كَاسُوَنْ سِڢٜىٰنْ دَ دُكَنْ غَرُرُوَنْتَ ذَاسُ تَمْبَيٜىٰكَ سُثٜىٰ «ذُوَانْكَ دُواْمِنْ كَڨُوثٜىٰ رَبُوانْ يَاڧِ نٜىٰ؟ دُوانْمٜىٰ كَتَتَّارَ سُواْجُواْجِنْكَ مَاسُيَوَ؟ دُواْمِنْ كَݣُوشِ أَظُرْڢَا دَ ظِينَارِيَ نٜىٰ؟ دُواْمِنْ كَتَڢِے دَ دَبُّواْبِے دَ كَايَيَّكِ نٜىٰ؟ دُواْمِنْ كَݣُوشِ رَبُوانْ يَاڧِ مَيْ يَوَنْ غَسْكٜىٰ نٜىٰ؟» ›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sheba da Dedan, da 'yan kasuwar Tarshish, da dukan garuruwa za su ce maka, ‘Ka zo kwasar ganima ne? Ko ka zo ka tattaro rundunarka don ka yi waso, ka kwashe azurfa da zinariya, da bisashe, da dukiya, ka kwashe babbar ganima?’