Ezekiel 4:14 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai na ce, “Ba haka ba ne, Ubangiji Mai Iko Duka! Ban taɓa ƙazantar da kaina ba. Daga ƙuruciyata har zuwa yanzu ban taɓa cin wani abin da aka samu ya mutu ko abin da namun jeji suka kashe ba. Ba nama marar tsabtan da ya taɓa shiga bakina.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ نَثٜىٰ «حَبَ! يَا عُبَنْ‌غِجِ يَهْوٜىٰهْ ، بَنْ تَٻَ ڧَظَنْتَرْ دَكَيْنَبَ؞ تُنْدَغَ ڧُرُثِيَتَ حَرْ ذُوَا يَنْذُ، بَنْ تَٻَ ثِنْ مُوشٜىٰ بَ، كُواْ أَبِنْدَ نَمُواْمِنْ دَاجِ سُكَ كَشٜىٰبَ؞ نَامَنْدَ يَضُٻَ مَا بَيْتَٻَ شِغُواْ بَاكِنَبَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai na ce, “Ya Ubangiji Allah, ban taɓa ƙazantar da kaina ba. Tun daga ƙuruciyata har zuwa yau, ban taɓa cin mushe ba, ko abin da namomin jeji suka kashe. Ƙazantaccen nama bai taɓa shiga bakina ba.”