Ezekiel 40:46 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
ɗaya ɗakin kuma da yake fuskantar arewa ne na firistocin da suke lura da bagade. Waɗannan su ne ’ya’yan Zadok maza, waɗanda su ne kaɗai Lawiyawan da za su iya yin kusa da Ubangiji don su yi hidima a gabansa.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
طَاكِنْ ثَنْ دَيَكٜىٰ ڢُسْكَنْتَرْ أَرٜىٰوَ، دُواْمِنْ ڢِرِسْتُواْثِے نٜىٰ وَطَنْدَ سُكٜىٰ دَ حَكِّنْ لُورَ دَ بَغَدٜىٰ؞ وَطَنَّنْ سُونٜىٰ دَغَ دَنْغِنْ ظَدُواكْ، سُو كَطَيْ نٜىٰ دَغَ ذُرِيَرْ لَوِ وَطَنْدَ ذَاسُذُواْ كُسَدَ يَهْوٜىٰهْ دُواْمِنْ سُيِ مَسَ حِدِمَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ɗakin da yake fuskantar arewa na firistoci ne waɗanda suke lura da bagade. Waɗannan su ne zuriyar Zadok waɗanda su kaɗai ne daga cikin Lawiyawa da suke da iznin kusatar Ubangiji don su yi masa hidima.”