Ezekiel 5:13 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Sa’an nan ne fushina zai huce hasalata a kanki kuma ta lafa, in kuma wartsake. Kuma sa’ad da na zuba fushina a kansu, a sa’an nan ne za su san cewa Ni Ubangiji na yi magana a cikin fushin kishina a kansu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«تَهَكَ ذَنْسَا ڢُشِنَ يَهُوثٜىٰ، ذَاڢِنْ ڢُشِنَ كُمَ ذَيْ سَوْكَ عَكَنْسُ، نِے كُمَ إِنْجِ سَوْكِ أَ رَيْنَ؞ سَعَدَّ ڢُشِنَ عَكَنْسُ يَڧَارٜىٰ، ذَاسُسَنِ ثٜىٰوَ نَيِ مَغَنَ سَبُواْدَ إِنَ بُڧَاتَرْ ثِكَكِّيَرْ ڧَوْنَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“‘Ta haka zan sa fushina ya huce, hasalata kuma a kansu ta lafa, ni kuma in wartsake. Sa'an nan za su sani ni Ubangiji na yi magana da zafin kishi sa'ad da na iyar da fushina a kansu.