Ezekiel 5:2 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’ad da kwanakin ƙawanyarka sun ƙare, sai ka ƙone kashi ɗaya bisa uku na gashin da wuta a cikin birnin. Ka ɗauki kashi ɗaya bisa uku ka yayyanka shi da takobi kewaye da birnin. Ka kuma watsar da kashi ɗaya bisa uku a iska. Gama zan fafare su da takobin da aka zāre.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَدَّ ݣُونَكِنْ دَ عَكَ كٜىٰوَيٜىٰ بِرْنِنْ دَ يَاڧِ سُنْثِكَ، ذَاكَ طَوْكِ كَشِ طَيَ نَغَاشِنْ كَڧُواْنٜىٰ دَ وُتَا أَڟَكِيَرْ بِرْنِنْ؞ كَشِ طَيَ كَايَيَّنْكَ دُكَ دَ تَكُواْبِے كَوَرْوَاڟَرْ دَشِ كٜىٰوَيٜىٰ دَ بِرْنِنْ؞ كَشِ طَيَ كُمَ ذَاكَ وَاڟَرْ عَ إِسْكَ؞ نِے كُوَ ذَنْبِے كَشِنَّنْ دَ تَكُواْبِے؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai ka ƙone kashi ɗaya da wuta a tsakiyar birnin sa'ad da kwanakin kewaye birnin da yaƙi suka cika. Ka kuma ɗauki sulusi ɗaya ka yanyanka da takobi kewaye da birnin. Sulusi ɗayan kuwa za ka watsar ya bi iska. Ni kuwa zan zare takobi a kansu.