Ezekiel 8:3 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya miƙa abin da ya yi kamar hannu ya kama a gashin kaina. Ruhu ya ɗaga ni tsakanin sama da ƙasa, a cikin wahayoyi kuma Allah ya ɗauke ni zuwa Urushalima, zuwa ƙofa zuwa gabas na cikin fili, inda gunki mai tsokanar kishi yake tsaye.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَمِيڧَ وَنِ أَبُ مَيْ كَامَ دَ حَنُّ، يَكَامَنِ تَغَاشِنْ كَيْنَ؞ رُوحُ كُمَ يَطَغَنِ ڟَكَانِنْ ڧَسَا دَ سَمَ؞ سَيْ يَكَٰوُاْنِ ثِكِنْ رُعُيَرْ اللَّهْ حَرْ ثِكِنْ عُرُوشَلِيمَ، يَبِے دَنِے تَڧُواْڢَرْ شِغَ ثِكِنْ ڢِيلِنْ غِدَنْ اللَّهْ وَنْدَ يَكٜىٰ ڢُسْكَنْتَرْ أَرٜىٰوَ، عِنْدَ صِڢَّ مَيْ تَيَرْدَ كِيشِنْ اللَّهْ تَكٜىٰ ذَمَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai ya miƙa hannu, ya kama zankon kaina. Ruhu kuma ya ɗaga ni bisa tsakanin sama da ƙasa, ya kai ni Urushalima cikin wahayi zuwa ƙofar farfajiya ta ciki, wadda take fuskantar arewa, inda mazaunin siffa ta tsokano kishi yake.