Ezekiel 8:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da suke yi, abubuwan banƙyamar da gidan Isra’ila ke yi a nan, abubuwan da za su kore ni daga wuri mai tsarkina? Amma za ka ga abubuwan da suka ma fi banƙyama.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَكُمَثٜىٰ «يَا كَيْ طَنْ مُتُمْ، يَنْذُ، كُواْ كَنَ غَنِنْ مَنْيَنْ أَبُبُوَنْ بَنْ ڨَمَرْ دَ غِدَنْ إِسْرَٰٓءِيلَ سُكٜىٰيِ أَنَنْ؟ سُنَيِنْ حَكَ دُواْمِنْ سُكُواْرٜىٰنِ إِنْيِ نٜىٰسَ دَغَ وُرِينَ مَيْ ڟَرْكِے؞ أَيْ، ذَاكَغَ مَنْيَنْ أَبُبُوَنْ بَنْ ڨَمَ ڢِيٜىٰدَ وَطَنَّنْ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da suke yi, abubuwa masu banƙyama da mutanen Isra'ila suke yi a nan don su kore ni nesa da Haikalina? Ai, za ka ga abubuwa masu banƙyama da suka fi haka.”