Ezekiel 9:3 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
To, fa, ɗaukakar Allah na Isra’ila ta haura daga bisa kerubobi, inda ta kasance, ta tashi zuwa bakin madogarar ƙofar haikali. Sai Ubangiji ya kira mutumin da yake saye da lilin wanda ya rataye jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَنْذُ ڧُنْشِنْ حَصْكٜىٰنْ طَوْكَكَرْ اللَّهْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ يَتَاشِ دَغَ كَنْ حَلِتُّو مَاسُ ڢِكَڢِكَيْ عِنْدَ دَا يَكٜىٰ ظَوْنٜىٰ، يَتَڢِے بَاكِنْ ڧُواْڢَرْ هَيْكَلِنْ؞ سَيْ يَهْوٜىٰهْ يَكِرَا مُتُمِنْ دَيَكٜىٰ سَنْيٜىٰ دَ رِغَرْ لِيلِنْ، وَنْدَ يَكٜىٰ رَاتَيٜىٰ دَ أَبِنْ رُبُوتُو أَغٜىٰڢٜىٰنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta tashi daga kan siffar kerubobi inda take zaune zuwa bakin ƙofar Haikalin. Sai Ubangiji ya kira mutumin da yake saye da rigar lilin, wanda yake rataye da gafaka.