Ezra 3:2 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Yeshuwa ɗan Yozadak da sauran firistoci, da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da abokan aikinsa, suka fara gina bagaden Allah na Isra’ila don miƙa hadaya ta ƙonawa bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa mutumin Allah.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يٜىٰشُوَ طَنْ يُواْظَدَكْ تَرٜىٰدَ یَنْعُوَنْسَ ڢِرِسْتُواْثِے دَ ظٜىٰرُبَّبٜىٰلْ طَنْ شٜىٰيَلْتِيٜىٰلْ تَرٜىٰدَ یَنْعُوَنْسَ سُكَ ڢَارَ غِنَا بَغَدٜىٰنْ اللَّهْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ؞ سُكَ غِنَا بَغَدٜىٰنْ دُواْمِنْ سُمِيڧَ هَدَايُ نَڧُواْنَاوَا بِسَغَ يَدَّ عَكَ رُبُوتَ عَثِكِنْ كُواْيَرْوَرْ مُوسَٰى مُتُمِنْ اللَّهْ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Yeshuwa ɗan Yehozadak tare da 'yan'uwansa, firistoci, da Zarubabel ɗan Sheyaltiyel tare da 'yan'uwansu, suka tashi suka gina bagaden Allah na Isra'ila domin a miƙa hadayu na ƙonawa kamar yadda aka rubuta a dokokin Musa, mutumin Allah.