Ezra 3:8 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A wata na biyu na shekara ta biyu, bayan sun komo gidan Allah a Urushalima, sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, Yoshuwa ɗan Yozadak da sauran ’yan’uwansa (Firistoci da Lawiyawa da duk waɗanda suka komo Urushalima daga bauta) suka fara aiki, aka zaɓi Lawiyawa daga masu shekaru ashirin da haihuwa zuwa waɗanda suka wuce haka don su dubi aikin ginin gidan Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَثِكِنْ وَتَ نَبِيُ نَشٜىٰكَرَا تَبِيُ بَايَنْدَ سُكَ إِسُواْ أَ غِدَنْ اللَّهْ أَ عُرُوشَلِيمَ، سَيْ ظٜىٰرُبَّبٜىٰلْ طَنْ شٜىٰيَلْتِيٜىٰلْ دَ يٜىٰشُوَ طَنْ يُواْظَدَكْ، تَرٜىٰدَ سَوْرَنْ یَنْعُوَنْسُ ڢِرِسْتُواْثِے دَ لَوِيَاوَا دَ كُمَ دُكَنْ وَطَنْدَ سُكَ كُواْمُواْ عُرُوشَلِيمَ دَغَ ڧَسَرْ بَوْتَا سُكَ ڢَارَ عَيْكِنْ؞ عَكَسَا لَوِيَاوَا مَاسُ شٜىٰكَرَا عَشِرِنْ ذُوَا سَمَ سُلُورَ دَ عَيْكِنْ سَاكٜىٰ غِنِنْ غِدَنْ يَهْوٜىٰهْ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A watan biyu na shekararsu ta biyu da suka komo wurin Haikalin Allah a Urushalima, sai Zarubabel ɗan Sheyaltiyel, da Yeshuwa ɗan Yehozadak, da sauran 'yan'uwansu firistoci, da Lawiyawa da dukan waɗanda suka komo Urushalima daga bauta suka fara aikin ginin. Suka sa Lawiyawa 'yan shekara ashirin zuwa gaba su yi shugabancin aikin ginin Haikalin Ubangiji.