Ezra 4:2 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
sai suka zo wurin Zerubbabel da kuma wurin shugabannin iyalai, suka ce, “Bari mu taimake ku ginin domin mu ma muna addu’a ga Allahnku yadda kuke yi, muna miƙa masa hadaya tun lokacin Esar-Haddon sarkin Assuriya wanda ya kawo mu nan.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سُكَجٜىٰ وُرِنْ ظٜىٰرُبَّبٜىٰلْ دَ كُمَ شُوغَبَنِّنْ دَنْ‌غِ دَنْ‌غِ سُكَثٜىٰ مُسُ «بَرِ مُهَطَكَيْ مُيِ غِنِنْ تَرٜىٰ، غَمَا مُو مَا مُنَيِ وَ اللَّهْ نْكُ سُجَّدَ كَمَرْ يَدَّ كُكٜىٰيِ؞ مُنْ دَطٜىٰ مُنَ مِيڧَ مَسَ هَدَايُ تُنْ زَامَانِنْ سَرْكِے عٜىٰسَرْهَدُّوانْ نَ أَسُّرِيَ وَنْدَ يَكَٰوُاْمُ نَنْ دَ ذَمَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
sai suka tafi wurin Zarubabel, da shugabannin gidajen kakanni, suka ce musu, “Ku yarda mana mu yi ginin tare, gama muna yi wa Allahnku sujada kamar yadda kuke yi, muna kuma ta miƙa masa sadaka tun kwanakin Esar-haddon, Sarkin Assuriya, wanda ya kawo mu nan.”