Ezra 7:6 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Shi Ezra ɗin ya zo daga Babilon. Shi malami ne ya kuma san Dokar Musa sosai wadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya bayar. Sarki ya ba shi duk abin da ya roƙa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
وَنَّنْ عُزَيْرُ نٜىٰ يَهَوْرُواْ دَغَ بَابِيلَ؞ شِ مَلَمِ نٜىٰ مَيْ ثِكَكّٜىٰنْ سَنِنْ كُواْيَرْوَرْ مُوسَٰى، وَدَّ يَهْوٜىٰهْ ، اللَّهْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ، يَبَا أَنَّبِے مُوسَٰى؞ سَرْكِے كُوَ يَبَا شِ دُكَنْ أَبِنْدَ يَضُواْڧَا، غَمَا حَنُّنْ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْسَ يَنَ تَرٜىٰ دَشِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ezra ɗin ya taho daga Babila. Shi malami ne, masanin shari'ar Musa, wadda Ubangiji Allah na Isra'ila ya bayar. Sarki kuwa ya ba shi dukan abin da ya roƙa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.