Ezra 9:1 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bayan an yi waɗannan abubuwa duka, sai shugabanni suka zo wurina suka ce, “Mutanen Isra’ila, har da firistoci da Lawiyawa ba su keɓe kansu daga maƙwabtansu ba, ba su kuma keɓe kansu daga irin rayuwar ƙazantar mutanen ƙasar ba, wato, rayuwar irinta Kan’aniyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Yebusiyawa, da Ammonawa, da Mowabawa, da Masarawa da Amoriyawa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَايَنْدَ عَكَيِ وَطَنَّنْ أَبُبُوَ، وَطَنْسُ دَتَّاوَنْ إِسْرَٰٓءِيلَ سُكَذُواْ وُرِينَ سُكَ غَيَ مِنِ إِرِنْ رَايُوَرْ دَ مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ دَ ڢِرِسْتُواْثِے دَ لَوِيَاوَا سُكٜىٰيِ؞ سُكَ كُمَ غَيَ مِنِ يَدَّ مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ بَسُ وَارٜىٰ كَنْسُ دَغَ ڧَبِيلُنْ ڧَسَرْ بَ، مَاسُ رَايُوَرْ ڧَظَنْتَا، وَتُواْ كَنْعَنِيَاوَا دَ هِتِّيَاوَا دَ ڢٜىٰرِظِّيَاوَا دَ يٜىٰبُسِيَاوَا دَ أَمُّواْنَاوَا دَ مُواْوَبَاوَا دَ مَصَرَاوَا دَ أَمُواْرِيَاوَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Bayan da aka gama waɗannan abubuwa, sai shugabanni suka zo wurina, suka ce, “Mutanen Isra'ila, da firistoci, da Lawiyawa ba su keɓe kansu daga ƙazantar mutanen ƙasar ba, wato su Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Yebusiyawa, da Ammonawa, da Mowabawa, da Masarawa, da Amoriyawa.