Ezra 9:2 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sun auro wa kansu da ’ya’yansu ’yan mata mutanen nan, ta haka aka kwaɓa zuriyar da aka tsarkake da ta mutanen nan da suke tare da su. Shugabanni da manyan ma’aikata su ne a gaba-gaba a aikata wannan abin kunya.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَمَا مَظَا نَ إِسْرَٰٓءِيلَ سُنْ عَوْرُواْ وَكَنْسُ مَتَ دَغَ ثِكِنْ ڧَبِيلُنْ ڧَسَرْ، حَرْ مَا سُنْ طَوْكُواْ وَیَیَنْسُ مَاتَادَغَ ثِكِنْسُ؞ تَهَكَ عَكَ ݣُوٻَ ذُرِيَرْ دَ عَكَ ڟَرْكَكٜىٰ دَ تَڧَبِيلُنْ ڧَسَرْ؞ شُوغَبَنِّ دَ دَتَّاوَا كُوَ سُنَدَ حَنُّ دُمُ دُمُ عَثِكِنْ عَيْكَتَ وَنَّنْ أَبِنْ كُنْيَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Gama sun auro wa kansu da 'ya'yansu 'yan matan mutanen nan. Yanzu tsattsarkar zuriya ta cuɗanya da mutanen ƙasashe. Shugabanni da magabata sun fi kowa laifi kan wannan rashin gaskiya.”