Galatians 3:8 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Nassi ya hanga cewa Allah zai kuɓutar da Al’ummai ta wurin bangaskiya, ya kuwa sanar wa Ibrahim wannan bisharar tun kafin lokaci yă yi cewa, “Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinka.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
رُبُوتَثِّيَرْ مَغَنَرْ اللَّهْ تَڢَطَا تُنْدَا ثٜىٰوَ وَطَنْدَ بَا يَهُودَاوَا بَذَاسُ عِيَ سَامُنْ مَڟَيِنْ أَدَلْثِے أَغَبَنْ اللَّهْ تَوُرِنْ بَنْغَسْكِيَ؞ سَبُواْدَ تُنْدَا مَا أَنْسَنَرْوَ إِبْرَٰهِيمْ لَابَرِ مَيْ دَاطِے ثٜىٰوَ «تَوُرِنْكَ نٜىٰ دُكَنْ أَلْعُمَّيْ ذَاسُ سَامِ أَلْبَرْكَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A cikin Nassi kuwa an hango, cewa Allah zai kuɓutar da al'ummai ta wurin bangaskiya, wato, dā ma can an yi wa Ibrahim bishara cewa, “Ta wurinka za a yi wa dukkan al'ummai albarka.”