Genesis 10:19 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَنْكِنْ ڧَسَرْ كَنْعَنِيَاوَا كُوَ يَا مِيڧٜىٰ كُدُ دَغَ سِدُوانْ ذُوَا غٜىٰرَرْ كُسَدَ غَاظَ، يَا كُمَ مِيڧٜىٰ غَبَسْ ذُوَا سُواْدُوامْ دَ غُواْمُواْرَ دَ أَدْمَ دَ ظٜىٰبُواْيِمْ كُسَدَ لَشَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yankin ƙasar Kan'aniyawa kuwa ya milla tun daga Sidon, har zuwa wajen Gerar, har zuwa Gaza, zuwa wajen Saduma, da Gwamrata, da Adma, da Zeboyim, har zuwa Lasha.