Genesis 13:10 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Lot ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, sai ya ga kwarin yana da ciyawa mai kyau ƙwarai sai ka ce lambun Ubangiji, kamar ƙasar Masar, wajajen Zowar. (Wannan fa kafin Ubangiji yă hallaka Sodom da Gomorra.)
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ لُوطُ يَطَغَ عِدَنُونْسَ، يَغَ ثٜىٰوَ ݣُورِنْ يُواْدَنْ حَرْ ذُوَا ذُواْوَرْ يَنَ ثِكٜىٰ دَ ثِيَوَرْ كِيوُاْ دَ وُرَارٜىٰنْ ضُوَ كَمَرْ غُواْنَرْ عَيْدَنْ وَدَّ يَهْوٜىٰهْ يَيِ، كُواْ كُمَ كَمَرْ ݣُورِنْ نِلُ أَ مَصَرْ؞ وَنَّنْ يَا كَسَنْثٜىٰ كَاڢِنْ يَهْوٜىٰهْ يَهَلَّكَ سُواْدُوامْ دَ غُواْمُواْرَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Lutu ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, ga shi kuwa da dausayi mai kyau ƙwarai, sai ka ce gonar Ubangiji, kamar ƙasar Masar wajen Zowar, tun kafin Allah ya hallaka Saduma da Gwamrata.