Genesis 15:13 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ وَ إِبْرَمْ «كَاسَنِ لَلَّيْ، ذُرِيَرْكَ ذَاسُيِ ذَمَنْ بَڧُنْثِ أَوَتَ ڧَسَرْدَ بَتَاسُبَ؞ عَثَنْ ذَاعَ سَا سُذَمَ بَايِ، ذَاعَيِ مُسُ دَنِّيَ حَرْ شٜىٰكَرَا طَرِے حُطُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani lalle ne zuriyarka za ta yi baƙunci cikin ƙasar da ba tata ba ce, za ta kuwa yi bauta, za a kuma tsananta mata har shekara arbaminya,