Genesis 17:19 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Allah ya ce, “Duk da haka dai, matarka Saratu za tă haifi maka ɗa; za ka kuma kira shi Ishaku. A kansa zan tabbatar da madawwamin alkawarina, da kuma ga zuriyarsa da za su zo bayansa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
اللَّهْ يَاثٜىٰ مَسَ «أَعَ، مَاتَرْكَ سَارَةُ ثٜىٰ ذَاتَ حَيْڢَ مَكَ طَا، ذَاكَ كِرَا سُونَنْسَ إِسْحَٰڧَ؞ ذَنْ كَڢَ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَتَ دَشِ، يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ تَهَرْ أَبَدَا دَشِ دَ ذُرِيَرْسَ دَ ذَاسُذُواْ بَايَنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Allah ya ce, “A'a, matarka Saratu ita ce za ta haifa maka ɗa, za ka raɗa masa suna Ishaku. A gare shi zan tsai da alkawarina madawwami, da kuma ga zuriyarsa a bayansa.