Genesis 19:17 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da suka fitar da su, sai ɗaya daga cikin mala’ikun ya ce, “Ku gudu domin ranku; kada ku duba baya, kada kuma ku tsaya ko’ina cikin kwarin! Ku gudu zuwa cikin duwatsu, don kada a hallaka ku!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَدَّ سُكَ ڢِتَرْدَسُو دَغَ بِرْنِنْ سَيْ سُكَثٜىٰ مُسُ «كُغُدُ دُواْمِنْ رَنْكُ! كَدَ كُوَيْوَيَ بَايَ، كُواْ كُڟَيَ كُواْعِنَ عَثِكِنْ ݣُورِ؞ كُغُدُ ذُوَا كَنْ تُدَّيْ دُواْمِنْ كَدَ أَ هَلَكَاكُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'ad da suka fitar da shi, suka ce, “Ka gudu domin ranka, kada ka waiwaya baya, ko ka tsaya ko'ina cikin kwari, gudu zuwa tuddai domin kada a hallaka ka.”