Genesis 20:9 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Abimelek ya kira Ibrahim ciki ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Ta wace hanya ce na yi maka laifi har da ka kawo irin wannan babban laifi a kaina da kuma masarautata? Ka yi mini abubuwan da bai kamata a yi ba.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَبِمٜىٰلٜىٰكْ يَا كِرَا إِبْرَٰهِيمْ وُرِنْسَ يَثٜىٰ «دُوانْمٜىٰ كَايِمَنَ حَكَ؟ وَنٜىٰ لَيْڢِے نَيِمَكَ دَ كَجَٰوُاْ مِنِ بَبَّنْ لَيْڢِے حَكَ عَكَيْنَ دَ يَنْكِنْ مُلْكِنَ؟ كَيِمِنِ أَبِنْدَ بَيْ كَمَاتَ عَيِبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Abimelek kuwa ya kira Ibrahim, ya ce masa, “Me ke nan ka yi mana? Wane laifi na yi maka, da za ka jawo bala'i mai girma haka a kaina da mulkina? Ka yi mini abin da bai kamata a yi ba.”