Genesis 21:12 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا اللَّهْ يَاثٜىٰ وَ إِبْرَٰهِيمْ «كَدَ كَدَامُ سَبُواْدَ يَرُوانْ دَ كُمَ بَيْوَرْكَ؞ كَسَوْرَرِ سَارَةُ، كَيِ دُكْ أَبِنْدَ تَڢَطَا مَكَ، غَمَا تَوُرِنْ إِسْحَٰڧَ نٜىٰ ذَاعَ لِسَّڢْتَا ذُرِيَرْكَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada zuciyarka ta ɓaci saboda yaron da kuma baiwarka. Kome Saratu ta faɗa maka, ka yi yadda ta ce, gama ta wurin Ishaku za a riƙa kiran zuriyarka.