Genesis 22:2 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَهْوٜىٰهْ يَا ثٜىٰمَسَ «طَوْكِ طَنْكَ إِسْحَٰڧَ، مَكَطَيْثِنْ طَنْكَ، وَنْدَ كَكٜىٰ ڧَوْنَ، سَيْ كُتَڢِے يَنْكِنْ مُواْرِيَ، كَمِيڧَشِ هَدَايَ تَڧُواْنَاوَا عَكَنْ طَيَ دَغَ ثِكِنْ مَنْيَنْ تُدَّنْ دَ ذَنْ نُونَ مَكَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya ce, “Ɗauki ɗanka, tilon ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi ƙasar Moriya, a can za ka miƙa shi hadayar ƙonawa a bisa kan ɗayan duwatsun da zan faɗa maka.”