Genesis 24:22 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’ad da raƙuman suka gama shan ruwa, mutumin ya fitar da zoben hanci na zinariya mai nauyin giram biyar da woroworo biyu na zinariya masu nauyin shekel goma, ya ba ta.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَدَّ رَاڧُمَنْ سُكَ غَمَ شَا، سَيْ مُتُمِنْ يَطَوْكِ ذُواْبٜىٰ مَيْ ڟَادَ نَظِنَرِيَ، يَسَا مَتَ أَهَنْثِ؞ يَا كَٰوُاْ مَنْيَنْ وَرْوَرُواْ غُدَا بِيُ يَا سَا أَ حَنُّوَنْتَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'ad da raƙuman suka gama sha, mutumin ya ɗauki zoben zinariya mai nauyin rabin shekel, ya sa mata a hanci. Ya kuma ɗauki mundaye biyu na shekel goma na zinariya ya sa a hannuwanta,