Genesis 24:30 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Nan da nan da ya ga zoben hancin da woroworo a hannuwan ’yar’uwansa, ya kuma ji Rebeka ta faɗa abin da mutumin ya ce mata, sai ya fita zuwa wurin mutumin, ya same shi yana tsaye wajen raƙuma kusa da rijiyar.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَبُواْدَ يَاغَ ذُواْبٜىٰنْ حَنْثِ دَ وَرْوَرُوانْ دَسُكٜىٰ أَ حَنُّوَنْ یَرْعُوَرْسَ رِڢْكَتُ دَ كُمَ يَدَّ يَجِ مَغَنَرْتَ ثٜىٰوَ «غَا أَبِنْدَ مُتُمِنْ يَڢَطَا مِنِ،» سَيْ يَتَڢِے وُرِنْ؞ يَا كُوَ سَامٜىٰشِ يَنَ ڟَيٜىٰ وَجٜىٰنْ رَاڧُمَنْ كُسَدَ رِجِيَرْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'ad da ya ga zoben da mundaye da suke hannuwan 'yar'uwarsa, sa'ad da kuma ya ji maganar Rifkatu 'yar'uwarsa cewa, “Ga abin da mutumin ya faɗa mini,” sai ya je wurin. Ya kuwa same shi yana tsaye wajen raƙuma kusa da rijiyar.