Genesis 24:7 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ubangiji Allah na sama, wanda ya fitar da ni daga gidan mahaifina, da kuma ƙasar asalina wanda kuma ya yi magana da ni, ya yi mini alkawari da rantsuwa cewa, “Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa, zai aika mala’ikansa yă sha gabanka domin ka samo wa ɗana mata daga can.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نَسَمَ، وَنْدَ يَڢِتَرْ دَنِے دَغَ غِدَنْ بَابَنَ دَ ڧَسَرْ حَيْڢُوَتَ، يَيِ مِنِ أَلْڧَوَرِ دَ ضَنْڟُوَا ثٜىٰوَ ذَيْبَا ظُرِيَاتَ ڧَسَرْ نَنْ؞ شِ يَهْوٜىٰهْ ذَيْ عَيْكِ مَلاَىِٕكَنْسَ كَاڢِنْ كَاإِسَ وُرِنْ؞ ذَاكَ كُوَ سَامُواْ وَ طَانَ مَتَ دَغَ ثَنْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji Allah na Sama wanda ya ɗauke ni daga gidan mahaifina daga ƙasar haihuwata, wanda ya yi magana da ni ya kuma rantse mini, ‘Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa,’ shi zai aiki mala'ikansa a gabanka. Za ka kuwa auro wa ɗana mata daga can.