Genesis 26:24 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A wannan dare Ubangiji ya bayyana gare shi ya ce, “Ni ne Allah na mahaifinka Ibrahim. Kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai, zan albarkace ka, zan kuma ƙara yawan zuriyarka saboda bawana Ibrahim.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ دَرٜىٰنَّنْ كُوَ يَهْوٜىٰهْ يَا بَيَّنَ غَرٜىٰشِ يَثٜىٰ مَسَ، «نِنٜىٰ اللَّهْ نَبَابَنْكَ إِبْرَٰهِيمْ؞ كَدَ كَجِڟُواْرُواْ، غَمَا نِے إِنَ تَرٜىٰدَكَيْ؞ ذَنْ كُمَ أَلْبَرْكَثٜىٰكَ، إِنْسَا ذُرِيَرْكَ سُيِيَوَ سَبُواْدَ بَاوَنَ إِبْرَٰهِيمْ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da daren nan Ubangiji ya bayyana gare shi ya ce, “Ni ne Allah na mahaifinka, kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai, zan sa maka albarka in riɓaɓɓanya zuriyarka saboda bawana Ibrahim.”