Genesis 27:29 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bari al’ummai su bauta maka mutane kuma su rusuna maka. Ka zama shugaba a kan ’yan’uwanka bari kuma ’ya’yan mahaifiyarka su rusuna maka. Bari waɗanda suka la’anta ka, su la’antu; waɗanda kuma suka sa maka albarka, su sami albarka.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَرِ ڧَبِيلُ سُيِ مَكَ حِدِمَ، أَلْعُمَّيْ كُمَ سُدُرْڧُسَ مَكَ؞ بَرِ كَذَمَ شُوغَبَنْ یَنْعُوَنْكَ، یَیَنْ مَامَرْكَ سُدُرْڧُسَ مَكَ؞ وَطَنْدَ سُكَ لَعَنْتَكَ، بَرِ أَلَعَنْتَسُ؞ وَطَنْدَ سُكَ أَلْبَرْكَثٜىٰكَ، بَرِ عَ أَلْبَرْكَثٜىٰسُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Bari jama'a su bauta maka, Al'ummai kuma su sunkuya maka. Za ka yi shugabancin 'yan'uwanka, Allah ya sa 'ya'yan mahaifiyarka su sunkuya maka. La'ananne ne dukan wanda ya la'anta ka, Albarkatacce ne dukan wanda ya sa maka albarka.”