Genesis 27:41 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Isuwa ya riƙe Yaƙub a zuciya saboda albarkar da mahaifinsa ya sa masa. Ya ce wa kansa, “Kwanakin mutuwar mahaifina sun yi kusa; sa’an nan zan kashe ɗan’uwana Yaƙub.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِسُوَ كُوَ يَاڧِ جِنِنْ يَعْڧُوبَ سَبُواْدَ أَلْبَرْكَرْ دَ بَابَنْسَ يَسَامَسَ؞ إِسُوَ يَيِ تُنَانِ ثٜىٰوَ «ݣُونَكِنْ مَكُواْكِنْ مُتُوَرْ بَابَنَ سُنْيِ كُسَ؞ سَعَنً ذَنْكَشٜىٰ طَنْعُوَنَ يَعْڧُوبَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Isuwa dai ya ƙi jinin Yakubu saboda albarkar da mahaifinsa ya sa masa. Sai Isuwa ya ce a ransa, “Kwanakin makoki domin mahaifina suna gabatowa, sa'an nan zan kashe Yakubu ɗan'uwana.”