Genesis 27:46 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Rebeka ta ce wa Ishaku, “Ni fa na gaji da matan Hittiyawan nan. In Yaƙub ya auri mata daga cikin matan ƙasan nan, wato, daga matan Hittiyawa irin waɗannan, rayuwata ba za tă daɗa mini kome ba.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ رِڢْكَتُ تَثٜىٰ وَ إِسْحَٰڧَ «نِے ڢَا نَاغَجِ دَ مَاتَا هِتِّيَاوَنَّنْ؞ عِدَنْ يَعْڧُوبَ شِيمَا يَا عَوْرِ طَيَ دَغَ ثِكِنْ وَطَنَّنْ، إِنَا أَمْڢَانِنْ رَيْنَ كُمَ أَغَرٜىٰنِ؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Rifkatu kuwa ta ce wa Ishaku, “Na gaji da raina saboda matan Hittiyawa. Idan Yakubu zai auri ɗaya daga cikin waɗannan mata na Hittiyawa, wato daga matan ƙasar, wane amfani raina zai daɗa mini?”