Genesis 33:13 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma Yaƙub ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ka san cewa ’ya’yan ƙanana ne, dole in lura da tumaki da shanun da suke shayar da jariransu. In aka kore su da gaggawa a rana guda kaɗai, dukan dabbobin za su mutu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا يَعْڧُوبَ يَثٜىٰ مَسَ «رَنْكَيَدَطٜىٰ، كَا سَنِ يَارَنْ بَاسُ دَ ڧَرْڢِے، كُمَ غَرْكُنَنْ تُمَكِ دَ أَوَكِ دَ نَشَانُو سُنَدَ ڧَنَانَا مَاسُ شَنْ مَامَا؞ عِدَنْ أَنْكُواْرٜىٰسُ رَانَ طَيَ كَيْ ڟَيٜىٰ، ذَاسُ مُمُّتُ دُكَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma Yakubu ya ce masa, “Shugabana, ai, ka sani 'ya'yan ba su da ƙarfi, ga kuma bisashe da shanun tatsa, ina jin tausayinsu ƙwarai da gaske. Idan kuwa aka tsananta korarsu kwana ɗaya, garkunan za su mutu duka.