Genesis 35:11 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
اللَّهْ يَثٜىٰ «نِنٜىٰ اللَّهْ مَيْ إِيكُواْ دُكَ ؞ كَيِ تَحَيْڢُوَ سُواْسَيْ كَيَلْوَتَ؞ أَلْعُمَّ دَ تَارُوانْ أَلْعُمَّيْ ذَاسُ ڢِتُواْ دَغَ غَرٜىٰكَ؞ سَرَاكُنَ كُمَ ذَاسُ ڢِتُواْ دَغَ ذُرِيَرْكَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka hayayyafa ka riɓaɓɓanya, al'umma da tattaruwar al'ummai za su bumbunto daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga cikinka.