Genesis 36:35 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’ad da Husham ya rasu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan da yaƙi a ƙasar Mowab, ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Awit.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ هُشَمْ يَمُتُ، سَيْ هَدَدْ طَنْ بٜىٰدَدْ، يَغَاجٜىٰشِ يَذَمَ سَرْكِے؞ وَنَّنْ هَدَدْ نٜىٰ يَثِ مِدِيَنَاوَا دَ يَاڧِ عَڧَسَرْ مُواْوَبْ؞ سُونَنْ بِرْنِنْسَ كُوَ أَوِتْ نٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da Husham ya rasu, sai Hadad ɗan Bedad wanda ya ci Madayana a ƙasar Mowab, ya ci sarauta a bayansa, sunan birninsa kuwa Awit ne.