Genesis 37:8 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai ’yan’uwansa suka ce masa, “Kana nufin za ka yi mulki a kanmu ke nan? Ko kuwa za ka zama sarki, a bisanmu?” Suka ƙara ƙin jininsa saboda mafarkinsa da kuma abin da ya faɗa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
یَنْعُوَنْسَ سُكَثٜىٰ «كَنَ نُڢِ ذَاكَ ذَمَ سَرْكِے عَبِسَنْمُ؟ كُواْ كُوَ ذَاكَيِ مُلْكِ عَكَنْمُ؟» سَيْ سُكَڧَارَ ڧِنْسَ سَبُواْدَ مَڢَرْكَنْسَ دَ كُمَ مَغَنْغَنُنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
'Yan'uwansa suka ce masa, “Ashe, lalle ne kai za ka sarauce mu? Ko kuwa, ashe lalle ne kai za ka mallake mu?” Sai suka daɗa ƙin jininsa domin mafarkansa da maganganunsa.